in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta yi alkawarin karfafa yin musaya da Sudan
2015-01-28 20:44:16 cri
Shugaban majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa na kasar Sin Yu Zhengsheng ya lashi takwabin karfafa dangantakar siyasa da musaya tsakanin jam'iyyun Sin da Sudan.

Yu ya bayyana hakan ne yau a nan birnin Beijing lokacin da yake ganawa da tawagar jam'iyyar NCP mai mulki a Sudan karkashin jagorancin mataimakin shugaban jam'iyyar kana mataimakin shugaban kasar Sudan Ibrahim Ghandour.

Mr Yu ya ce, a ko da yaushe JKS da gwamnatin kasar Sin suna daukar dangankatar kasashen biyu da muhimmancin gaske. Sannan kasar Sin za ta ci gaba da nuna gaskiya tare da kokarin kare moriyarsu yayin da take bunkasa dangantaka da kasashen Afirka.

A nasa jawabin Ibrahim Ghandour ya ce, Sin sahihiyar abokiyar Sudan ce, kuma yana fatan kasarsa za ta yi koyi da nasarorin da Sin ta samu yayin da take kara zurfafa musaya tsakanin kasashen da kuma jam'iyyunsu da ke mulki. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China