in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 551 ne suka mutu sakamakon abkuwar rikici a Yemen
2015-04-25 17:11:28 cri
A jiya Jumma'a ne kakakin babban kwamishinan kula da harkokin hakkin bil'adama na MDD Rupert Colville, ya bayyana cewa, rikicin kasar Yemen ya haddasa mutuwar mutane 551 tsakanin ranar 26 ga watan Maris zuwa 22 ga watan Afrilun kadai, cikin wannan adadi kuwa hadda mata 31, da kuma yara kananan 115, yayin da kuma wasu mutane su 1185 suka jikkata, baya ga gine-gine 64 da aka lalata.

A daya hannun kuma, ofisoshin MDD a Yemen, ciki hadda ofishin babban kwamishinan kula da harkokin hakkin bil'adam na MDD a kasar, su ma sun lalace sakamakon harin sama da aka rika kaddamarwa.

Asusun yara na MDD ya tabbatar da cewa, a kalla yara kananan 140 ne aka shigar cikin dakarun soja a Yemen, yayin da aka mamaye makarantu 30, aka kuma kai hari kan asibitoci 23.

Game da wannan batu, hukumar kiwon lafiya ta duniya ta furta cewa a yanzu haka, dukkanin asibitocin dake Yemen suna fama da karancin magunguna.

Tun dai daga karshen watan Maris din da ya gabata ne hadaddiyar rundunar sojin kawance da kasar Saudiyya ke jagoranta ta fara kai hare-hare ta sama kan sansanonin dakarun Ḥūthi dake kasar ta Yemen, wanda hakan ya yi sanadiyyar mutuwar mutane da dama, yayin da wasu kuma suka yi gudun hijira.

Bisa alkaluman da aka bayar, an ce, a kalla mutane dubu 150 ne suke gudun hijira sakamakon wannan rikici. (Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China