in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin tana maraba da kawo karshen harin sama a Yemen
2015-04-22 20:46:22 cri
Kasar Sin tayi maraba da kawo karshen harin sama da ake kaima kasar Yemen a kan dakarun Houthi, tare da yin kira da a yi sulhun siyasa a kasar.

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hong Lei yace Sin tana fatan dukkan bangarorin zasu aiwatar da yarjejeniyar kwamitin sulhun MDD da kungiyar hadin gwiwar kasashen yankin Gulf wato GCC, su koma kan teburin shawarwari ba tare da bata lokaci ba.

Mr Hong Lei yace hakan zai samar da mafita na siyasa da zai tafi da yanayin da kasar ta Yemen ke ciki tare da kula da dukkan wadanda hakan ya shafa wanda a ganin kasar Sin zai kawo daidaito da ikon a hukumance ga kasar cikin lokaci. Kakakin ya fadi haka ne a tyayin da yake bayani ga manema labarai a laraban nan game da shawarar kasar Saudiya da kawayenta na dakatar da kai harin sama a kasar ta Yeman.(Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China