in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi girgizar kasa mai karfi a Nepal
2015-04-25 17:10:44 cri

Wata girgizar kasa ta auku a birnin Kathmandu fadar mulkin kasar Nepal, kamar yadda shafin yanar gizo na sakwannin girgizar kasa na hukumar binciken yanayin kasa dake Amurka ya ambata.

Sakon dai na nuna cewa girgizar kasar mai karfin digiri 7.9 bisa ma'aunin Richter, ta auku ne a Asabar din nan, ta kuma haddasa lalacewar wasu gine-gine. Sai dai kawo yanzu ba a kai ga tantance yawan mutanen da suka rasu, ko wadanda suka jikkata ba.

Baya ga gine-gine da suka lalace, an ce girgizar kasar ta kuma barnata turakun sadarwar wayar tarho dake birnin.

Rahotanni sun bayyana cewa an ji tasirin wannan girgizar kasa a arewa da tsakiyar India, amma babu rahoton rasuwa ko jikkatar mutane. Kaza lika an dakatar da zirga-zirgar jiragen kasa na karkashin kasa a birnin New Delhin kasar India na dan lokaci. Amma ance yanzu haka an ci gaba da gudanar da sufuri ta layin dogon kamar yadda aka saba.

Baya ga yankin India, an ji tasirin wannan girgizar kasa a Malaysia da Bangladesh, da ma wasu sassan jihar Tibet na nan kasar Sin.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China