in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Girgizar kasa ta shafi mutane dubu 14 a lardin Yunnan na kasar Sin
2014-12-07 17:10:45 cri
A jiya Asabar 6 ga watan nan ne ma'aikatar harkokin jama'ar kasar Sin ta fidda wani bayani ta shafin yanar gizo, game da yanayin da ake ciki dangane da bala'un girgizar kasa, da suka aukawa gundumar Jinggu dake lardin Yunnan.

Bayanin ya nuna cewa ya zuwa daren jiya, girgizar kasar mai karfin digiri 5.8 da 5.9 bisa ma'aunin Richter, ta shafi mutane dubu 14 a birnin biranen Puer da Lincang, yayin da wani mutum guda ya rasa ransa, baya ga wasu mutanen 15 da suka jikkata.

Kaza lika kididdiga ta nuna cewa dakuna 36 na gidaje iyalai 12 sun rubta, yayin da wasu dakunan 1033 na gidaje iyalai 224 334 suka yi matukar lalacewa. Sai kuma wasu dakunan 2411 na gidaje iyalai 804 da suka dan tabu. A kuma halin yanzu ana ci gaba da nazari kan halin da ake ciki a yankunan da wannan annoba bala'in ta ya aukawa.

Wakilinmu ya ce ya yin taron manema labaru da hukumar lura da girgizar kasa ta lardin Yunnan din ta gudanar da misalin karfe 9 na daren jiya, dukkanin bala'un biyu, tasiri ne na girgizar kasar da ta abku a ranar 7 ga watan Okbota, wadda karfin ta ya kai digiri 6.6 bisa ma'aunin Richter. A wannan karo dai, ba ya ga jikkatar mutane, girgizar kasar ta haifar da lalacewar manyan ababen more rayuwa, kamar hanyoyi, da bututun samar da ruwan sha da dai sauransu.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China