in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Alexander Adjei ya lashe lambar yabo a gasar kwallon rairayi ta hukumar CAF
2015-04-23 09:36:10 cri
Dan wasan kwallon rairayi daga kasar Ghana Alexander Adjei, ya samu nasarar lashe lambar yabo, ta dan wasa mafi nuna bajimta, a yayin gasar kwallon rairayi wadda hukumar kwallon kafar Afirka ta CAF ke shiryawa.

Adjei ya samu nasarar cin kwallaye 16, a gasar da ta gudana a kasar Seychelles, an kuma zabe shi a matsayin gwarzon dan wasan ne, bayan da ya buga wa kasar sa wasanni 4, duk kuwa da cewa kulaf din da yake wakilta wato Black Sharks na kasar Ghana, bai samu nasarar lashe gasar ta wannan karo ba.

Wannan ne dai karon farko da kungiyar ta Black Sharks ta samu zarafin shiga wannan gasa, inda ta zamo a matsayi na 7, yayin da sauran kasashen Afirka 8 suka fafata a gasar.

Da yake tsokaci game da nasarar da dan wasan kulaf din sa ya samu, cokin kasar ta Ghana Daniel Kotey, ya ce sun koyi darussa da dama a gasar ta Seychelles, irin darussan da za su basu damar karfafa kwarewar su a nan gaba.

Kasar Madagascar ce dai ta lashe kofin na bana, bayan da ta ci dukkanin wasannin da ta buga a gasar. Yanzu haka kuma Madagascar da kasar Senegal ne za su wakilci nahiyar Afirka, a gasar kwallon rairayi ta duniya wadda hukumar FIFA za ta shirya a kasar Portugal.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China