Riffo ya bayyanawa wani taron manema labaru cewa, a halin yanzu, hanyoyin motoci a yankin arewacin kasar Chile sun lalace a sakamakon bala'in, musamman hanyoyin motoci dake birnin Copiapo dake yankin Atacama, don haka ba bu tabbacin karbar bakuncin gudanar gasar tseren motoci ta Dakar a wannan yanki na kasar a shekarar dake tafe.
A 'yan kwanakin baya ne bala'in ambaliyar ruwa ya aukawa manyan yankuna 3 dake arewacin kasar Chile, wanda ya yi matukar lalata gine-gine, da hanyoyin motoci, da gadoji da sauran ayyukan more rayuwa. Har wa yau mutane 26 sun rasa rayukan su sakamakon bala'in, yayin da kuma mutane 125 suka bace. (Zainab)