in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tunisia: Sin na iya taka muhimmiyar rawa game da hadin gwiwar kasashen Asiya da Afirka
2015-04-21 10:15:04 cri
Wakilin shugaban kasar Tunisia, kuma shugaban sashen nahiyar Asiya da Amurka, a ma'aikatar harkokin wajen kasar Elyes Kasri, wanda ke halartar taron ministoci a taron shugabannin kasashen Asiya da Afirka, ya ce kasar Sin da kasashen Afirka suna da kyakkyawar dangantaka, kuma Sin na iya taka muhimmiyar rawa wajen inganta hadin gwiwar dake tsakanin sassan biyu.

Kasri wanda ya bayyana hakan a taron dake gudana a birnin Jakarta dake kasar Indonesia ya kuma kara da cewa, yanzu haka kasashen Afirka suna samun bunkasuwa cikin sauri, kana suna kokarin koyi daga fasahohin kasashen Asiya. A daya hannun kuma kasar Sin da kasashen Afirka, suna kiyaye kyakkyawar dangantaka, yayin da Sin ke taka muhimmiyar rawa wajen bunkasa hadin gwiwar dake tsakanin Asiya da Afirka.

Daga nan sai ya bayyana kyakkyawar alakar dake tsakanin kasarsa da kasar Sin, kasashen da ya ce suna sada zumunta tsawon lokaci. Kaza lika ya bayyana aniyar kasar Tunisia, ta kara inganta kawancen dake tsakaninta da kasar Sin, tare da gudanar da shawarwari a tsakanin sassan biyu, musamman game da batun hadin gwiwa tsakanin Afirka da kasar ta Sin. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China