in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta dage kan manufar rashin yin shisshigi game da harkokin cikin gidan kasashen Afrika
2015-04-20 09:28:27 cri
Manzon musamman na kasar Sin mai lura da harkokin nahiyar Afrika Zhong Jianhua, ya bayyana cewa, a har kullum kasar Sin na ci gaba da taimakawa kasashen Afrika wajen raya tattalin arziki, tana kuma dora muhimmanci sosai game da aikin wanzar da zaman lafiya da tsaro a yankin, a hannu guda kuma, kasar ta Sin na nacewa bin manufar rashin tsoma baki a harkokin cikin gidan kasashen nahiyar ta Afrika.

Mista Zhong ya fadi hakan ne, a 'yan kwanakin baya, yayin da yake zantawa da manema labaru a birnin Yaounde, hedkwatar kasar Kamaru. Kaza lika, ya gabatar da ra'ayinsa game da batutuwan da ke haifar da kalubale game da aikin shimfida zaman lafiya da tsaro a Afrika, kamar batun Sudan ta Kudu, da rikicin Somaliya, da na kasar Mali da kuma kasar Kongo (kinshasa).

Wakilin na Sin ya kuma sake nanata cewa, kamata ya yi al'ummar Afrika ta warware batutuwan da suke shafe bisa dabaru irin nata. Yayin da Sin ke ganin dacewar amfani da kungiyar AU, da sauran kungiyoyin shiyya-shiyya da kasashen da rikicin ya shafa kansu don warware matsalolin Afrika. (Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China