in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhu na M.D.D. ya tsaida kudurin kara yawan sojojin kiyaye zaman lafiya dake Afrika ta Tsakiya
2015-03-27 14:35:10 cri
Bisa kudurin da kwamitin sulhu na M.D.D. ya tsayar a jiya Alhamis ranar 26 ga wata, an ce, an amince da kungiyar M.D.D ta wanzar da lafiya a kasar Afrika ta Tsakiya ta kara sojojinta 750, da 'yan sanda 280, da jami'ai 20.

A wannan rana, kwamitin sulhu na M.D.D. ya yi taro game da halin da ake ciki a Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya, inda aka zartas da wani kuduri cewa, bisa bukatar sakatare-janar na M.D.D. Ban Ki-moon, ban da kiyaye yawan 'yan kungiyar da aka tanada cikin kuduri mai lamba 2149, za a kara tura wasu zuwa wannan kasa.

An ce, Ban Ki-moon ya mika wa shugaban kwamitin sulhu na M.D.D.wata wasika a ranar 29 ga watan Janairu na bana, inda ya bayyana cewa, ganin yanayin rashin tabbas da ake ciki a Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya, da rikicin da ke ci gaba a tsakanin dakarun fararen hula masu aikin sa kai ta fuskar aikin tsaro Anti-Balaka da tsohon 'yan kungiyar Seleka, ana bukatar karin sojoji don tabbatar da tsaro.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China