in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Afrika ta kudu ta dauki niyyar kiyaye tsaron baki
2015-04-18 16:02:54 cri

Gwamnatin Afrika ta Kudu za ta yi iyakacin kokarinta domin kiyaye tsaron dukkan 'yan kasar da 'yan kasashen waje da ke cikin kasar, in ji shugabannin tawagogin diplomasiyya na kasashen Afrika a ranar Jumma'a a birnin Pretoria. Da take jawabi a gaban jami'an diplomasiyya domin yi musu bayani kan matakan da Afrika ta kudu ta dauka domin kawo karshen hare haren kyamar baki da a yanzu haka ke shafar 'yan kasashen waje dake wannan kasa, musammun ma kuma 'yan Afrika bakar fata, ministar harkokin wajen kasar Afrika ta Kudu, madam Maite Nkoana-Mashabane, ta bayyana cewa kasarta ta tsaya tsayin daka wajen kare martaba da darajar dan Adam da girmama kasa mai 'yanci. (Maman Ada)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China