in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin na fatan za a kai ga samun ci gaba a shawarwari na gaba kan nukiliyar Iran
2015-04-17 20:12:06 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hong Lei, ya ce Sin na fatan za a kai ga samun ci gaba, don gane da shawarwarin da za a koma kan nukiliyar kasar Iran.

Mr. Hong, wanda ya bayyana hakan yayin wani taron manema labaru a Jumma'ar nan, ya kara da cewa Sin za ta ba da dukkanin gudummawa, domin cimma nasarar da aka sanya gaba, a zagayen shawarwarin da za a gudanar a ranekun 22 da 23 ga watan nan a birnin Vienna.

A ranar 2 ga watan nan ne dai kasashe 6 da batun nukiliyar Iran ya shafa da ita kanta Iran din, suka cimma matsaya game da matakan da za a dauka a yayin shawarwarin da za a gudanar na gaba, shawarwarin da ake fatan za su ba da damar kaiwa ga cimma matsaya, nan da ranar 30 ga watan Yuni mai zuwa.

Mr. Hong ya kara da cewa daga yanzu zuwa wannan wa'adi, za a gudanar da tattaunawa kan muhimman batutuwa, don haka Sin ke fatan dukkanin sassan da wannan batu ya shafa za su dauki matakan da suka dace, domin samun nasarar shawarwarin.

Tuni dai aka sanar da cewa wakilai a fannin siyasa na kasashen da wannan batu ya shafa, za su gudanar da taruka na kwanaki biyu, a wani mataki na kokarin cimma matsaya guda. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China