in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin na fatan samun ci gaba a sabon zagayen tattauna game da nukiliyar kasar Iran
2014-12-16 20:31:08 cri
Kasar Sin ta bayyana kudurinta na taka muhimmiyar rawa wajen ganin an cimma yarjejeniya a sabon zagayen tattaunawar da za a fara ranar Laraba game da shirin nukiliyar kasar Iran a birnin Geneva.

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Qin Gang ne ya bayyana hakan yau yayin taron manema labarai a nan birnin Beijing.

Kasar Sin ta bukaci sassan da abin ya shafa, da su yi kokarin cimma wata yarjejeniyar da za ta kawo karshen wannan batu cikin ruwan sanyi.

Qing Gang ya ce, babban darektan sashen hana yaduwar makamai na ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Wang Qun ne zai jagoranci tawagar kasar Sin a wannan tattaunawa.

Kasar Iran da manyan kasashen duniya sun amince su kara wa'adin tattanauwar ce zuwa ranar 30 ga watan Yunin shekara ta 2015, don kara samun lokaci da damar cimma madafa.

Idan ba a manta ba a ranar 24 ga watan Nuwamba ne bangaren Iran da manyan kasashen duniya 6 da wannan batu ya shafa suka cimma wata yarjejeniya bayan an gaza cimma kwakkwarar matsaya. A karkashin kwarya-kwaryar yarjejeniyar, Iran ta amince ta dakatar da wasu ayyukanta na nukiliya domin a sassauta mata takunkumin da aka kakaba mata. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China