in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin tana adawa da ganawa tsakanin Obama da Dalai Lama
2015-02-02 20:28:51 cri
Kasar Sin ta jaddada kin amincewarta da kowane shugaban kasa ya gana da Dalai Lama ta kowane fuska, inji kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar a ranar litinin din nan.

Hong Lei a ganawarsa da manema labarai a madadin gwamnatin kasar Sin yace ba a yarda ba ta kowane hali ga wata kasa ta tsoma baki cikin al'amuran cikin gida kasar da ya shafi Tibet.

Wannan lafazin na shi ya biyo bayan yiwuwar ganawa ne tsakanin shugaban kasar Amurka Barrack Obama da Dalai Lama a ranar alhamis mai zuwa 5 ga wata domin karin kumallon safe.

Mr Hong yace abinda ya shafi Tibet ya shafi kasar Sin da harkokin cikin gidanta don haka Sin ke kira ga Amurka da ta tsaya a kan matsayinta game da Tibet da kuma warware abin da ya shafi hakan don amfanan dukkan bangarori tsakanin Sin da ita kanta Amurkan.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China