in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin na fatan ganin an kara baiwa kasashe masu tasowa damar samun wakilci da ikon bayyana ra'ayi
2015-04-13 20:37:07 cri

Kasar Sin na goyon bayan aikin kwaskwarima game da tsarin kwamitin sulhun MDD, da kuma fatan ganin an baiwa kasashe masu tasowa karin wakilci, da ikon bayyana ra'ayi.

Hakan na kunshe ne cikin kalaman kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hong Lei, yayin da yake jawabi gaban mahalarta taron manema labaru da ake saba shiryawa a nan Beijing.

Mr. Hong ta kara da cewa aiwatar da kwaskwarima a tsarin kwamitin tsaron MDD ya shafi fannoni da dama, wanda hakan ke da alaka da bunkasar MDD cikin tsahon lokaci, da kuma moriyar dukkan kasashe mambobinta.

Ya ce har kullum kasar Sin na tsayawa tsayin daka game da burin cimma daidaito kan batutuwa daban daban, ta hanyar shawarwari bisa dimokuradiyya, wanda kuma sassa daban daban ke halarta, matakin da ya kasance tamkar ainihin burin kasar Sin dangane da yi wa kwamitin sulhun gyaran fuska.

Kaza lika kasar Sin na kallon MDD a matsayin wata babbar hukuma. Don hakan baya ga aiwatar da kwaskwarima ga kwamitin sulhun, MDDr na bukatar gudanar da gyare-gyare a fannonin zamantakewar al'ummar kasashen duniya da batun samar da ci gaba. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China