in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin za ta karbi shugabancin kwamitin sulhu na MDD na wannan karo
2015-02-04 10:30:55 cri
A jiya ne zaunannen wakilin Sin dake MDD Liu Jieyi ya sanar a cibiyar MDD dake birnin New York cewa, kasar Sin za ta karbi shugabancin kwmaitin sulhu na MDD na wanan karo a watan Febrairu, kana ya yi kira da a gudanar da muhawara kan tabbatar da zaman lafiya da tsaro a kasashen duniya.

A ranar 3 ga wata da safe ne, a matsayinsa na shugaban kwamitin sulhu na watan Febrairu, Liu Jieyi ya shugabanci taron kwamitin, daga baya ya gudanar da taron manema labaru, inda ya yi bayani kan ayyukan kwamitin na wannan wata. Liu Jieyi ya ce, kwamitin sulhun zai gudanar da taruruka fiye da 20 a watan Febrairu, wadanda suka shafi batutuwa kimamin 20, kana za su tattauna kan batutuwan da suka fi jawo hankalin kasashen duniya da ke faruwa a Syria, Gabas ta Tsakiya, Iraki, Yemen, Guinea Bissau, Somaliya, Sudan ta Kudu da dai sauransu.

Ban da wannan kuma, Liu Jieyi ya bayyana cewa, shekarar bana shekara ce ta cika shekaru 70 da kafa MDD da nasarar yaki da fascist a duniya. Don haka, kasar Sin ta yi kira da a gudanar da muhawara a tsakanin ministocin kasashe mambobin kwamitin sulhun bisa taken "tabbatar da zaman lafiya da tsaro, da duba tarihi da koyi da fasahohi da kuma jaddada alkawarin da aka yi na martaba ka'idojin tsarin MDD", kuma ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ne zai shugabanci muhawarar. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China