in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta dare kujerar jagorancin kwamitin sulhu na MDD na wannan karo
2013-11-02 17:03:11 cri
A ranar Jumma'a daya ga wata, kasar Sin ta zama jagorar kwamitin sulhu na MDD na wannan karo, bisa wa'adin aiki da zai kai zuwa karshen wannan wata na Nuwamba.

Zaunannen wakilin Sin a MDDr Liu Jieyi ne ya bayyana hakan, yana mai cewa, bisa tsarin da ake kai yanzu, za a yi tarurruka da shawarwari sama da 20 a wannan wata, wadanda suka shafi batutuwa kimanin 20, don gane da harkokin kasashen Afirka da na yankin Gabas ta Tsakiya masu matukar muhimmanci.

Liu ya ce, a matsayin ta na shugaban kwamitin sulhun MDD a wannan karo, Sin za ta yi mu'amala da hadin gwiwa da sauran membobin kwamitin sulhun, da ma bangarori daban daban bisa adalci a bayyane, tare da yin kokari kan daidaita harkokin shiyya-shiyya, dake janyo hankali, tare da sa kaimi wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaron duniya.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China