in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin na kokarin ciyar da tsarin dokokin kasa da kasa gaba
2015-04-13 20:11:32 cri
Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Sin Liu Zhenmin ya bayyana cewa, taron bana na kungiyar tattaunawa game da harkokin doka tsakanin kasashen Asiya da Afirka karo na 54 ya nuna aniyar Sin game da cimma alkawarin da ta yi na karfafa tsarin dokokin kasa da kasa gaba.

Mr. Liu wanda ya bayyana hakan a Litinin din nan a wajen bikin bude taron, ya kara da cewa Sin na burin yin hadin gwiwa da sauran kasashen Afirka, da kuma kafa sabbin dangantakar kasa da kasa bisa tushen hadin gwiwa da cimma moriyar juna.

Ya ce, gwamnatin kasar Sin na mai da hankali kwarai da gaske wajen gudanar da harkokin kasa bisa dokoki da kuma ciyar da tsarin dokokin kasa da kasa gaba, tana kuma fatan inganta wannan aiki a yayin gudanar taron na wannan karo.

A daya bangaren kuma, kasar Sin na mai da hankali sosai ga hadin gwiwa tare da kasashe masu tasowa wajen bunkasa harkokin kasa da kasa da na shiyya-shiyya, baya ga burinta na karfafa hadin gwiwa da kasashen Asiya da Afirka, karkashin wannan dandali na taron kungiyar tattaunawar harkokin doka na Asiya da Afirka. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China