in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bangaren yawon bude ido na Zimbabwe ya bukaci a soke haraji
2015-04-12 15:47:42 cri
Hukumar yawon bude ido ta kasar Zimbabwe (ZTA) ta bayyana cewa ta yin matsin lamba kan gwamnatin kasar na ta soke haraji kan yawon bude ido da ya kai kashi 15 cikin 100, wanda a cewarta tushe ci gaban wannan bangare. Muna kokarin ganawar da gwamnati kan yadda wannan matsala ke shefar wannan bangare idan aka ci gaba da karbar haraji, in ji darektan zartarwa na ZTA, mista Karikoga Kaseke.

A cikin watan Janairu, gwamnatin Zimbabwe ya tilasta biyan haraji ga otel otel din kasar dake karbar masu yawon shakatawa daga kasashen waje, lamarin da ya gurguntar da ci gaban bangaren yawo bude ido sosai.

Karbar wannan haraji ya maida kasar Zimbabwe yankin mafi tsada a fannin yawon shakatawa a lokacin da kasar ke bukatar janyo hankalin masu yawon bude ido wanda kuma yawansu ya ragu sosai a tsawon shekaru goma na baya bayan nan, in ji masu ruwa da tsaki a fannin harkokin yawon bude ido. A lokacin baya, ba a biya haraji kan wurin kwana da sauran ayyuka ga masu yawon bude ido daga kasashen waje. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China