in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi ganawa tsakanin manyan jami'an soja na Sin da Zimbabwe
2014-10-11 10:03:58 cri
A jiya Juma'a 10 ga wata, mataimakin shugaban kwamitin aikin sojan kasar Sin, Fan Changlong ya gana da ministan tsaro na kasar Zimbabwe Sydney Sekeramayi a nan birnin Beijing.

A yayin ganawar, Fan Changlong ya ce, tun bayan da aka kulla huldar diplomasiya tsakanin Sin da Zimbabwe, dangantakar dake tsakanin kasashen biyu na samun ci gaba yadda ya kamata, kuma manyan jami'ai na kara kai wa juna ziyara. Ya kara da cewa, kasar Sin na mayar da hankali sosai kan hadin kai a dukkan fannoni tsakanin rundunonin sojojin kasashen biyu.

A nasa bangaren, Sydney Sekeramayi ya bayyana cewa, ana ta gudanar da hadin kai mai inganci tsakanin kasashen biyu ta fuskar aikin tsaro, don haka ya yi fatan za a karfafa yin cudanya da hadin kai tsakanin rundunonin sojojin kasashen biyu a nan gaba. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China