in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Amurka ya sanar da tsawaita wa'adin aikin takunkumin da aka sanyawa kasar Somaliya
2015-04-09 10:11:55 cri
Shugaba Barack Obama na Amurka ya sanar da tsawaita wa'adin aikin takunkumin da aka sanyawa kasar Somaliya da shekara daya, takunkumin da a yanzu wa'adinsa zai kammala a watan Afrilun shekara mai zuwa.

Obama ya ce halin da ake ciki a Somaliya na barazana ga tsaron kasar Amurka,da manufofinta na harkokin waje, don haka aka tsawaita wa'adin dokar-ta-baci, da takunkumin dake kan kasar wanda ya fara aiki tun a watan Afrilun shekarar 2010.

A shekarar 2010 ne dai shugaba Obama ya ba da umurnin sakawa wasu mutane, da kungiyoyin kasar ta Somaliya takunkumi, kana a watan Yulin shekarar 2012, ya sanar da hana fitar da charcoal daga cikin kasar. Daga baya kuma aka kara sakawa Somaliyar karin takunkumi, wanda ya shafi wasu mutane, da kungiyoyin kasar masu barazana ga wanzuwar zaman lafiya, da ayyukan ba da gudummawar jin kai.

Gwamnatin Obama ta bayyana cewa, fitar da charcoal daga kasar Somaliya na iya samar da kudin shiga mai yawa ga kungiyar masu tsattsauran ra'ayi ta Al-Shabaab dake kasar. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China