in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Somaliya ta tabbatar da mutuwar wani babban jami'in kungiyar Al Shabaab a harin sama da sojojin kasar Amurka suka kai
2015-02-05 10:49:36 cri
Hukumomin kasar Somaliya sun tabbatar a jiya cewa, wani babban jami'in kungiyar masu tsattsauran ra'ayi ta Al Shabaab da ke kasar ya mutu a hari ta sama da sojojin kasar Amurka suka kai a ranar 31 ga watan Janairu.

Hukumar leken asiri da tsaron kasar Somaliya ta bayar da sanarwa a wannan rana, inda ta bayyana cewa, sojojin kasar Amurka sun kai hari ta sama kan sansanin mayakan kungiyar Al Shabaab dake kudancin kasar Somaliya a ranar 31 ga watan Janairu, kuma shugaban kungiyar dake kula da harkokin gudanar da ayyuka da leken asiri Yusuf Dheeq da wasu manyan jami'an kungiyar sun mutu a sakamakon harin.

Sanarwar ta kara da cewa, Yusuf Dheeq yana da hannu a hare-hare da dama da aka kai a kasar ta Somaliya.

Har zuwa yanzu dai, kungiyar Al Shabaab ba ta bayar da wata sanarwa game da hari ta sama da sojojin Amurka suka kai ba. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China