Cikin wata sanarwar da aka rabawa manema labarai a birnin Fatakwal fadar mulkin jihar ta Rivers, sakataren gwamnatin jihar George Feyii ya bukaci daukacin al'ummar jihar da su kiyaye wannan doka, yana mai cewa an kafa ta ne domin tabbatar da doka da oda, tare da kaucewa barkewar rikici.
A jiya Litinin ne dai dandazon mata magoya bayan jam'iyyar adawar APC suka yi jerin gwano sanye da bakaken kaya, suka kuma dunguma ofishin hukumar zaben kasar INEC reshen jihar, domin mika korafi game da abun da suka kira magudin zaben da aka tafka a jihar, sai dai kafin isar su ofishin na INEC ne 'yan sanda suka harba musu barkonon tsohuwa, nan take kuma suka tarwatse tawagar. (Saminu Hassan)