in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An ci gaba da shawarwari game da batun nukiliyar Iran
2015-03-27 11:04:05 cri
Bayan da dan hutu na tsawon kwanaki 5, a jiya Alhamis ranar 26 ga wata, bangarori 6 da batun nukiliyar kasar Iran ya shafa, wato Amurka, Birtaniya, Faransa, Rasha, Sin da kuma Jamus, sun sake taro a birnin Lausanne da ke kasar Switzerland, don cimma matsaya guda gabanin wa'adin karshe na watan nan na Maris.

A safiyar jiyan ne,sakataren harkokin wajen Amurka John Kerry, da takwaransa na kasar Iran Javad Zarif, suka gudanar da shawarwari har na tsawon sa'o'i 2 da rabi,wanda ya samu halartar ministan kula da harkokin makamashin Amurka Ernest Moniz, da na hukumar makamashi ta Iran Ali-Akbar Saleh, da ma sauran wakilan Turai. Daga bisani kuma, wakilan bangarorin shida su ma za su yi shawarwari a tsakanin bangarorin biyu-biyu da kuma bangarorin daban daban.

Bisa labarin da aka bayar, an ce, idan komai ya gudana yadda ya kamata, ministocin harkokin wajen kasashen bangarori 6 za su shiga tattaunawar.

A matsayin shawarwari karo na 5, baya ga bangarorin daban daban da ke da ra'ayi guda game da dage shawarwarin, ana ganin cewa shawarwarin na wannan karo sun zamanto wani taro mai muhimmanci.

Yayin da wani babban jami'in diplomasiyya dake halartar shawarwarin ke zantawa da wakilinmu, ya ce, yanzu abubuwan da ke janyo ka-ce-na-ce cikin shawarwarin su ne, yadda za a tabbatar da hakkin Iran wajen yin amfani da makamashin nukiliya don zaman lafiya, da yadda kasashen duniya za su amince da Iran, a fannin raya makamashin nukiliya domin bunkasa ayyukan zaman lafiya kadai.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China