in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan kasar Iraki ya ce, an shiga matakin karshe na yakin da aka yi a jihar Salahudin
2015-03-26 16:41:30 cri
Firaministan kasar Iraki Haider al-Abad, ya ce an shiga matakin karshe na aikin soja da sojojin kasar suka yi a jihar Salahudin mai kusanci da tsakiya da arewacin kasar.

Al-Abad ya bayyana hakan yayin da yake jawabi a gidan telebijin mallakar kasar a daren jiya Laraba.

A daya hannun kuma shugaban kwamitin tsaron majalisar dokokin jihar Salahudin ya bayyanawa 'yan jarida cewa, jiragen saman yaki na kasar Iraki, sun kaddamar da hari kan sansanin dakarun kungiyar IS dake yankin gabashin birnin Tikrit, musamman a gabar kogin Tigris, da kuma wurin dake kewaye da fadar tsohon shugaban kasar Saddam Hussein, bisa taimakon jiragen sama na kawancen kasa da kasa kan yaki da kungiyar IS.

An ce harin ya lalata dakuna da dama da aka ajiye makamai a cikin su, da kuma motocin soja masu dauke da manyan makamai, baya ga mutane da dama, da kuma mayakan kungiyar ta IS wadanda suka rasa rayukan su. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China