in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi kira da a rika yiwa mata adalci a fannin halartar wasannin motsa jiki
2015-03-26 14:24:05 cri
Hukumar harkokin mata ta MDD, da kwamitin wasannin Olympics na duniya wato IOC, sun gudanar da taron tattaunawa mai taken "hange makoma- rawar da wasanni suke takawa wajen samar da iko ga mata bayan shekarar 2015", inda aka yi kira da a samar da dama mai inganci ga mata wajen halartar wasannin motsa jiki.

Tsohuwar 'yar wasan gudun kankara daga kasar Amurka Michelle Kwan, ta yi jawabi yayin taron, ta na mai cewa lokacin da mata ke shiga wasannin motsa jiki, da harkokin zamantakewar al'umma, da bada ilmi a makarantu, da kuma takara a ayyukansu, za su iya kara taimakawa wajen kirkiro hanyoyin inganta zamantakewar al'umma mai karfi, da zaman karko.

Kana Kwan ta bayyana cewa, kara samar da iko ga mata ta hanyar shiga wasannin motsa jiki, bai tsaya ga samar musu da na'urorin wasanni kawai ba, har ma da samar musu da damar cimma burinsu yadda ya kamata.

Shekarar bana dai shekara ce ta cika shekaru 20 da gudanar da babban taron mata na duniya, kuma MDD za ta gudanar da wasu ayyuka na kira ga samar da adalci ga mata, da baiwa mata iko da damar samun bunkasuwa.(Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China