in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan tsaron Amurka ya yi alkawarin ci gaba da taimakawa sojojin Afghanistan zuwa karshen 2017
2015-03-24 16:09:25 cri
Ministan tsaron Amurka Ashton Carter, ya bayyana kudurin ma'aikatarsa, na ci gaba da samar da kudaden tallafi ga sojojin tsaron Afghanistan, har ya zuwa karshen shekarar 2017. Kana kuma ma'aikatar za ta bukaci majalisar dokokin kasar da ta kebe kudaden da ake bukata domin wannan aiki.

Mr. Carter ya bayyana hakan ne a yayin taron manema labaru da aka shirya a sansanin David, inda shugaban kasar ke hutu a wannan rana. Ya ce, domin tabbatar da tsaron kasar Afghanistan, kwamandan sojojin hadaka na Afghanistan da na kasashen waje, ya ba da shawarar tabbatar da aikin sojojin Afghanistan da yawansu ya kai dubu 352. Ya kuma yi imani da cewa, karancin sojoji a kasar zai kawo babbar hasara ga Afghanistan da sauran kawancen kasashen, don haka ya bayyana muhimmancin ci gaba da hadin gwiwa tsakanin Amurka da sauran kasashen duniya, wajen tabbatar da yawan sojojin da ake bukata a kasar cikin dogon lokaci.

Har wa yau, a gun taron manema labaru da aka gudanar, sakataren harkokin wajen Amurka John Forbes Kerry, ya sanar da cewa, za a bude wani sabon shirin hadin gwiwa tsakanin gwamnatocin Amurka da Afghanistan, don yin amfani da kudin agaji da yawansu ya kai dalar Amurka miliyan 800 wajen tantance, da sa kaimi ga cimma burin yin gyare-gyare ga gwamnatin Afghanistan, da kuma habaka ci gaban kasar. (Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China