in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Manzon musamman na shugaban Sin ya halarci bikin rantsar da sabon shugaban kasar Afghanistan
2014-09-30 10:09:24 cri
A ranar 29 ga wata, manzon musamman na shugaban kasar Sin Xi Jinping kuma ministan kwadago da bada tabbaci ga zaman rayuwar al'ummar kasar Sin Yin Weimin ya halarci bikin rantsar da sabon shugaban kasar Afghanistan Ashraf Ghani Ahmadzai da aka gudanar a birnin Kabul, kana ya gana da sabon shugaban kasar Ghani.

Yin Weimin ya isar da sakon taya murnar shugaban kasar Sin Xi Jinping ga Ghani da ya zama sabon shugaban kasar Afghanistan, kana ya bayyana cewa, kasar Sin tana maraba ga kasar Afghanistan da ta kafa gwamnatin hadin gwiwa da za ta kunshi dukkan al'ummun kasar, kana tana fatan kasar za ta samu hadin kan al'umma da zaman lafiya a karkashin jagorancin shugaba Ghani. Har wa yau kuma, kasar Sin za ta ci gaba da taimakawa kasar Afghanistan wajen sake shimfida zaman lafiya.

A nasa bangare,shugaba Ghani ya nuna godiya ga manzon musamman na shugaba Xi Jinping da ya halarci bikin rantsar da shi, kana ya bukaci Yin Weimin da ya isar da gaisuwarsa zuwa ga shugaba Xi Jinping. Ghani ya bayyana cewa, sabuwar gwamnatin sa tana dora muhimmanci ga zumunta da hadin gwiwa a tsakaninta da kasar Sin, tare da dangantakar dake tsakaninsu. Kasar Afghanistan tana fatan kasar Sin za ta ci gaba da nuna goyon baya gare ta wajen shimfida zaman lafiya, da taka muhimmiyar rawa wajen warware matsalolin da kasar Afghanistan ke fuskanta. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China