in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Saliyo ta sanar da dokar hana fita ta kwanaki uku a fadin kasar
2015-03-22 16:38:02 cri
Kasar Saliyo ta sanar da matakin tsawaita dokar hana fita ta tsawon kwanaki uku a dukkan fadin kasar da zummar kawo karshen annobar cutar Ebola. Gwamnatin kasar Saliyo ta bayyana a ranar Alhamis cewa zata kafa dokar hana fita ta tsawon kwanaki uku a babban birnin kasar da kuma arewacin kasar daga ranar 27 zuwa 29 ga watan Maris.

Shugaban kasar Saliyo Ernest Bai Koroma ya bada umurni a ranar Asabar ta hanyar kafofin rediyo da talabajin na kasar ga al'ummar kasar baki daya dasu tsaya gidajensu a tsawon wannan lokaci, a matsayin wata hanyar neman kawar da cutar Ebola kwata kwata daga wannan kasa.

Mista Koroma ya kuma bayyana cewa ranakun 4, 11 da 18 ga watan Afrilu a matsayin ranakun tsaya wa gida domin baiwa fararen hula damar sanya hannu cikin kokarin da ake na cimma burin ba bu mutum ko guda mai dauke da cutar Ebola.

A tsawon wannan lokaci na hana fita, ba za a gudanar da harkokin kasuwanci ba a dukkan fadin kasar. Sai dai ma'aikatan lafiya, masu aikin sa kai a yayin kamfen, jami'an tsaro da kuma manema labarai kadai ne zasu rika kaiwa da kawowa. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China