in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Saura kiris a ayyana Liberia a matsayin kasar da ta shawo kan cutar Ebola
2015-03-14 16:41:49 cri
Shugaban shirin dakile yaduwar Ebola a kasar Liberia Tolbert Nyenswah, ya ce nan da ranar 13 ga watan Afirilun dake tafe, hukumar lafiya ta duniya WHO za ta ayyana kasar Laberia, a matsayin wadda ta samu nasarar kawo karshen cutar Ebola, muddin ba a sake samun wani wanda ya kamu da cutar ba.

Mr. Nyenswah ya ce yanzu haka an kwashe kwanaki 18, tun bayan samun mutum na karshe da ya kamu da cutar a gundumar Montserrado, gundumar da a baya ta kasance wurin da aka fi samun yaduwar cutar.

Ya ce wasu gundumomin kasar sun kai makwanni 3 ko fiye, ba tare da samun sabbin masu kamuwa da Ebola ba.

Duk da wannan nasara da ake ci gaba da samu a sassan kasar, mai magana da yawun shirin yaki da cutar na MDD a Laberian Lisa white, ta ja hankalin al'ummar kasar da su yi taka-tsantsan, kasancewar iyakokin Laberia da kasashen dake ci gaba da yaki da cutar na bude a yanzu haka.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China