in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mazauna birnin Lagos na samun binciken lafiya da magunguna kyauta
2015-03-21 15:56:53 cri
Kungiyar Arise Women, kungiya ce mai zaman kanta a Najeriya, da ta rarraba magunguna kyauta ga mazauna birnin Lagos.

A kalla yara da manya kusan dubu daya ne suka samu binciken lafiya da magunguna kyauta da suka hada da binciken idanu da rarraba tabarau na kara gani, binciken lafiya da ba da jinya kyauta, tare da kuma binciken cutar cancer, hawan jini, yawan suga cikin jini da sauransu.

Siju Iluyomade na kungiyar Arise Women ya bayyana cewa wadannan ayyukan binciken lafiya da bada magunguna kyauta ana yinsu ne domin taimakawa al'ummomin da ba su da kudi zuwa asibiti idan suna fama da cutar suga ko ta hawan jini.

Mista Iluyomade ya bayyana cewa ayyukan kungiyarsa na da manufar bunkasa aikin bada jinya ta rigakafi tun daga tushe.

Mista Adebayo Olasubomi, wani mauzauni da ya samu gajiyar wannan aiki, ya bayyana cewa wadannan ayyuka na bada jinya kyauta za su karfafa kiwon lafiyar mazauna jihar, domin yawancinsu mutane ne da ba su da karfin ganin likita. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China