in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yawan mutanen da rikici ya halaka a duniya a shekarar 2014 ya karu da kashi 28 cikin 100
2015-03-19 10:39:58 cri
A jiya ne wata hukumar nazari ta fidda wani rahoto da ke cewa, yawan mutanen da suka rasu sakamakon rikicin da ya barke a duniya a shekarar 2014 ya karu da kashi 28 cikin 100 bisa na shekarar 2013, wannan lamari ya fi kamari a kasar Siriya, inda yawan mutanen da suka mutu a kasar ya kasance a kan gaba cikin shekaru 2 a jere.

Bayan da aka nazarci kididdigar da M.D.D. da sojojin Amurka da hukumar kare hakkin dan Adam ta Siriya suka bayar, hukumar ta bayyana cewa, mutane kimanin dubu 76 ne suka mutu a kasar Siriya a shekarar 2014 sakamakon rikicin.

Bisa labarin da aka bayar, an ce, rikicin na da alaka da kungiyar masu tsattsauran ra'ayin addinin Islama. Kana rikicin da ya barke tsakanin gwamnatin Iraki da kungiyar ISIS ya yi sanadiyyar mutuwar mutane dubu 21. A kasar Afghanistan kuma, wannan adadi ya kai 14638, yayin da yawan mutanen da suka mutu a Najeriya ya kai 11529.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China