in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An tattauna game da rahoton aikin kotun koli ta jama'ar kasar Sin da na babbar hukumar gabatar da kara ta kasar.
2015-03-12 15:09:17 cri

An yi cikakken zama karo na 3 na taron shekara-shekara na majalissar wakilan jama'ar kasar Sin a yau Alhamis din nan, domin nazari da tattaunawa, kan rahoton aikin kotun koli ta jama'ar kasar Sin, da na babbar hukumar gabatar da kara ta kasar.

Taron ya samu halartar shugaba Xi Jinping da Firaminista Li Keqiang da shugaban majalisar Zhang Dejiang da kuma sauran shugabannin kasar Sin.

Shugaban kotun kolin jama'ar kasar Sin Zhou Qiang, ya gabatar da rahoto game da manyan ayyuka na shekarar bara, da shirin tafiyar da ayyuka na shekarar 2015 a fannin aikin kotun koli. Har wa yau shugaban babbar hukumar gabatar da kara ta kasar Sin Cao Jianming, shi ma ya gabatar da rahoto game da manyan ayyuka na shekarar bara, da muhimman ayyuka na shekarar 2015 na sashensa. (Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China