in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jami'an kasashen Afirka sun jinjinawa rahoton aiki na gwamnatin kasar Sin
2015-03-05 14:45:49 cri

A wajen taron karo na 3 na majalisar wakilan jama'ar kasar Sin ta 12 da aka bude a yau, firaministan kasar Sin mista Li Keqiang ya gabatar da rahoto kan ayyukan da gwamnatin kasar ta yi a shekarar 2014, gami da shirin aikinta a shekarar 2015, ga dukkan wakilan jama'ar kasar Sin, jakadu na kasashe daban daban, gami da kafofin yada labarun kasar Sin da na ketare.

Jakadan kasar Ghana dake kasar Sin, mista Anani Demuyakor, wanda ya halarci taron, ya ce rahoton da firaministan kasar Sin ya gabatar yana da kyau sosai, domin ya bayyana hakikanin yanayin da kasar Sin take ciki. Haka kuma a cewar jakadan Ghana, niyyar da kasar Sin ta dauka wajen yaki da cin hanci da rashawa, gami da kokarin raya tattalin arzikinta a shekarar 2015, ta burge shi kwarai da gaske. Ban da haka kuma, ya ce karuwar tattalin arzikin kasar Sin, bisa matsayinta na wata babbar kasa mai babbar kasuwa, za ta amfanawa kasashen Afirka.

1 2 3
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China