in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen duniya sun jinjinawa kasar Sin bisa gudummawar wajen yaki da cutar Ebola
2015-03-04 15:32:10 cri
Manyan jami'ai mahalarta taro game da cutar Ebola, sun jinjinawa kasar Sin, bisa gudummawar da ta baiwa kasashen Afirka wajen yaki da cutar Ebola, suna masu bada shawara ga bangaren masu bada gudummawa na kasa da kasa, da su ci gaba da goyon bayan kasashen yammacin Afirka, wajen sake raya tattalin arzikin su, da zamantakewar al'umma bayan an kai ga dakile cutar.

A jiya Talata ne dai aka gudanar da taron, karkashin hadin gwiwar kungiyar EU, da kasar Liberia, da Saliyo, da Guinea, da kungiyar AU, da kungiyar ECOWAS, da kuma MDD a birnin Brusels na kasar Belgium.

Cikin jawabin da ya gabatar ministan harkokin wajen kasar Saliyo Samura Kamara, ya ce kasar Sin kasa ce ta farko dake taimakawa kasar Saliyo wajen yaki da cutar Ebola. Kuma ya zuwa yanzu Sin ta riga ta samar da gudummawa har karo hudu ga kasar Saliyo, ciki har da tallafin kudi, da na'urorin kiwon lafiya, da motoci, da likitoci da dai sauransu.

Shi kuwa babban jami'in hukumar zartaswa ta kwamitin tallafin bala'in fari na Oxford dake Birtaniya Mark Goldring, cewa ya yi kasashe 3 na yammacin Afirka da cutar tafi shafa suna kokarin amfani da taimakon da kasashen duniya ke basu. Kuma kasar Sin da kasashen uku za su iya yin hadin gwiwa, wajen tsara shiri game da yadda za a bunkasa fannonin kiwon lafiya, da bada ilimi, da harkokin aikin gona, da tattalin arziki da dai sauransu, kana da batun yin amfani da tallafin da suke samu yadda ya kamata. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China