in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan harkokin waje na Sin ya jagoranci muhawara kan zaman lafiya da tsaro
2015-02-24 20:12:45 cri

A jiya ne ministan harkokin wajen Sin Wang Yi ya jagoranci muhawarar kwamitin sulhun MDD kan tabbatar da zaman lafiya da tsaro a duniya a birnin New York, hedkwatar MDD, yayin bikin murnar cika shekaru 70 da nasarar yaki da Fascist a duniya da kuma murnar cika shekaru 70 da kafa MDD.

Wang ya bayyana cewa, makasudin yin wannan muhawarar a yau shi ne, na farko, koyon darasi daga tarihi, da nanata alkawarin da aka yi kan kundin tsarin mulkin MDD, na biyu, kokarin samar da makoma mai kyau, da neman samun wata sabuwar hanya a fannin tabbatar da zaman lafiya da tsaro a duniya a cikin sabon yanayi.

A wannan rana, ban da jagorantar muhawarar kwamitin sulhu, Wang Yi ya kuma gana da takwarorinsa na Malaysia Anifah Aman, da na Rasha Sergei Lavrov, da babban sakataren MDD Ban Ki-moon, da shugaban babban taron MDD Sam Kahamba Kutesa da sauransu. Abu mafi muhimmanci shi ne, ya isar da wani muhimmin sako a fili, wato Sin tana kokarin tabbatar da tsarin duniya mai kwanciyar hankali, tare da kokarin kiyaye shi, a maimakon kawo masa kalubale.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China