in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta ba da muhimmiyar gudummawa ga kasashen yammacin Afirka wajen yaki da cutar Ebola
2015-02-15 15:42:42 cri
Kakakin tawagar MDD ta musamman kan yaki da cutar Ebola Fatoumata Fatoumata Lejeune-Kaba ta bayyana wa wakilin kamfanin Xinhua a birnin Accra dake kasar Ghana a kwanakin baya cewa, yayin da kasashen yammacin Afirka suke fama da matsalar cutar Ebola, gwamnatin kasar Sin ta samar musu da gudummawar kayayyaki cikin sauri, ciki har da na'urorin ba da kariya, kana ta tura likitoci da dama zuwa kasashen, kuma ta ce, Sin ta taka muhimmiyar rawa wajen yaki da cutar Ebola.

A kokarin da ake na kara karfin ayyukan MDD, da gudanar da ayyukan hana yaduwar cutar Ebola, ba da jinya ga masu kamu da cutar, da yin rigakafin cutar ne, aka kafa tawagar MDD ta musamman kan yaki da cutar a watan Satumba na bara. Wannan shi ne karo na farko da MDD ta kafa wata tawagar tinkarar matsalar da ta shafi kiwon lafiya, kuma cibiyarta na birnin Accra dake kasar Ghana.

Kaba tana fatan kasashen duniya, ciki har da kasar Sin za su ci gaba da ba da gudummawa ga kasashen yammacin Afirka har zuwa lokacin da za a kawo karshen cutar ta Ebola. Kaba ta kuma bayyana cewa, Sin tana iya taimakawa kasashen yammacin Afirka masu fama da cutar Ebola, ta yadda za su sake inganta matakansu na kiwon lafiya, musamman a kasashen Saliyo da Liberia, da kuma kara yin hadin gwiwa a tsakaninta da kasashen a fannin kiwon lafiya bayan da aka kawar da cutar don kara inganta karfinsu na tinkarar cututtuka masu yaduwa a nan gaba. A cewarta, Sin ta taba samun sakamako a wannan fanni. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China