in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Afrika ta Kudu na da niyyar kawar da zazzabin cizon sauro kwata kwata daga kasar
2014-04-26 16:11:13 cri
Kasar Afrika ta Kudu ta samu muhimmin ci gaba kan kokarin da take na rage hadarun zazzabin cizon sauro da ma kawar da wannan cuta kwata kwata daga kasar nan da shekarar 2018, in ji gwamnatin Afrika ta Kudu a ranar Jumma'a a yayin bikin ranar zazzabin cizon sauro ta duniya.

Hakan na da nufin dakatar kawar da kamuwa da cutar kwata kwata daga al'ummomin kasar baki daya, in ji ministan kiwon lafiya a cikin wata sanarwar da aka fitar albarkacin ranar yaki da zazzabin cizon sauro ta duniya da aka yi bikinta ranar 25 ga watan Afrilu.

Ministan kiwon lafiyan Afrika ta kudu ya yi amfani da wannan rana ta yaki da zazzabin cizon sauro ta duniya domin mai da hankali kan cimma ayyuka, ci gaban da aka samu da matsalolin da ake fuskanta yayin dake yaki da wannan cuta a cikin kasar da ma wajen kasar, musammun ma a cikin shiyyar kungiyar SADC, in ji mista Popo Maja, kakakin ma'aikatar kiwon lafiya ta kasar.

Dalilin tsare tsaren kasa da na gundumomi na sanya ido kan cutar zazzabin cizon sauro, kasar Afrika ta Kudu ta samu nasarar rage cutar zazzabin cizon sauro a cikin kasar, tare da adadin masu dauke da kwayoyin cutar dubu 60 a shekarar 2000 zuwa matsakaicin adadin kimanin dubu 7 a kowace shekara.

Cutar zazzabin cizon sauro a Afrika ta Kudu na zuwa bisa yanayin lokaci kuma ta fi shafar yankunan kasar kamar Limpopo, Kwazulu-Natal da Mpumalanga. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China