in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Guinee ya isa Afrika ta Kudu domin halartar bikin rantsar da Jacop Zuma
2014-05-24 16:00:51 cri
Shugaban kasar Guinee Alpha Conde na a yanzu haka a kasar Afrika ta Kudu domin halartar bikin rantsar da Jacob Zuma, shugaban kasar Afrika ta Kudu da aka sake zabensa a baya bayan nan a matsayin shugaban kasar, a cewar wata sanarwar cibiyar watsa labarai ta fadar shugaban kasar Guinee.

A cewar wannan sanarwa, Alpha Conde ya isa kasar Afrika ta Kudu bisa gayyatar takwaransa na Afrika ta Kudu.

Tawagar gwamnatin Guinee na karkashin jagorancin shugaba Conde ta tashi daga birnin Conakry da sanyin safiyar ranar Jumma'a 23 ga watan zuwa Pretoria, babban birnin Afrika ta Kudu.

Bikin rantsar da shugaba Jacob Zuma, ya biyo bayan sake zabensa a matsayin shugaban kasar bisa wani sabon wa'adi na shekaru biyar.

A yayin zabubukan na ranar 7 ga watan Mayun da ta gabata, Jacob Zuma ya samu kashi 62,15 cikin 100 na kuri'un zabe tare da samun rinjayen yawan kujeru 249 cikin 400 na majalisar dokokin kasar. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China