in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An fara zabe a kasar Afirka ta kudu
2014-05-07 20:32:11 cri
Yau ne aka fara zabe a kasar Afirka ta kudu wanda shi ne karo na 5 tun bayan shekara ta 1994, inda hukumomi a kasar suka ce an fara shi yadda ya kamata ko da yake an samu wasu 'yan matsaloli nan da can.

An bude sama da kashi 90 cikin 100 na cibiyoyin zaben kasar 22,360 da karfe 7 na safe, amma ba a bude wasu a kan lokaci ba saboda matsalolin kayan aiki da na ma'aikata.

Babban jami'in hukumar zaben kasar mai zaman kanta (INEC) Mosotho Moepya ya shaida wa manema labarai cewa, zaben ya gudana cikin kwanciyar hankali da lumana a yankin Pretoria, sai dai an fuskanci zaman dar-dar a Bekkersdal da kudancin Johannesburg, bayan da aka kona wasu rumfunan zabe guda 2 ranar Talata da dare.

Sai dai kakakin gwamnatin kasar Phumla Williams ya sanar da cewa, an dauki matakan tsaro don tabbatar da cewa, an gudanar da zaben cikin lumana. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China