in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta gargadi Japan game da dokar tsaron da ta ke son yiwa gyaran fuska
2015-02-13 20:25:17 cri
Kasar Sin ta bukaci Japan da ta yi hattara kan dokar tsaronta da take son yiwa gyaran fuska, bayan da firaministan na Japan Shizo Abe ya gaza yin bayani game da abubuwan da ke kunshe cikin dokar.

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying ce ta bayyana hakan yau yayin taron manema labarai a nan birnin Beijing.

Ta ce, Sin na fatan Japan za ta waiwayi tarihi kan irin abubuwan da ta aika a baya ba tare da wata rufa-rufa ba, sannan ta amince kan abubuwan da ta aikata wanda haka ne kadai zai sa Japan din ta samu wata makoma mai haske.

Madam Hua ta kuma bukaci Japan da ta yi la'akari kan sassan soja da tsaro a lokacin da take aiwatar da wadannan gyare-gyare sannan ta kasance mai bin turbar neman ci gaba cikin lumana da bunkasuwar yankin baki daya.

A jiya ne firaminista Abe a lokacin da yake jawabi a majalisar dokokin kasar ya jaddada shirinsa na yin gyaran fuska ga bangarorin aikin gona, ayyukan kiwon lafiya, shirin samar da tsaron jama'a, Ilimi da kuma tattalin narziki, sai dai bai yi bayani game da batun dokar tsaron da ake saran za a tattauna a zaman majalisar na wannan shekara ba. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China