in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta canza zuwa kasar da ke sa hannu a harkokin tsara dokokin haraji na duniya
2015-02-11 15:31:57 cri
A jiya Talata 10 ga watan nan, shugaban sashen kula da harkokin haraji na kasa da kasa, na hukumar kula da harkokin haraji ta kasar Sin Liao Tizhong, ya bayyana cewa a yanzu haka kasar Sin ta shiga jerin kasashen dake da hannun cikin tsara dokokin da suka shafi haraji a duniya, a maimakon matsayin ta na baya na koyi da sauran kasashen duniya.

A cewar Mr. Liao, hakan ya alamanta ci gaban da kasar ta Sin ta samu a fannin sanya hannun cikin tsarin dokokin tattalin arzikin duniya.

Liao Tizhong wanda ya bayyana hakan a gun taron manema labarai da cibiyar nazarin harkokin haraji ta duniya ta kasar Sin ta shirya, dangane da "manyan harkokin haraji guda 10 na duniya a shekarar 2010", ya kara da cewa, dokokin haraji na duniya suna da muhimmin matsayi a fannin dokokin tattalin arzikin duniya.

Yace a yayin da take sa hannu cikin harkokin tsara dokokin haraji na duniya, kasar Sin tana kuma mai da hankali a kan tabbatar da adalci, da kuma taimaka wa kasashe masu tasowa, da masu karamin karfi wajen shiga aikin inganta kwarewarsu ta fannin gudanar da harkokin haraji.

"Dole ne a yi la'akari da moriyar kasashe masu tasowa, da ma masu karancin kudin shiga, ya kamata a taimakawa juna, da hada kai da juna, domin tabbatar da jituwa a duniya.", in ji Liao Tizhong.(Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China