in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yawan kudin da gwamnatin kasar Sin ta kebe wa aikin soja ya yi kasa da matsakaicin yawan kudin soja na kasashen duniya
2015-02-12 20:21:31 cri
Bisa "rahoton daidaita karfin soja na kasashen duniya na shekarar 2015" da cibiyar kasar Burtaniya da ke nazarin manufar aikin soja ta kasa da kasa ta fitar a ranar Laraba 11 ga wata, an ce, a cikin 'yan shekarun nan, kasar Sin ta shiga sabon yanayi na kera jiragen ruwan yaki da yawa, yawan kudin da gwamnatin kasar Sin ta kebe wa aikin soja ya karu sosai, amma ba ta bayyana hakan ba.

Game da wannan rahoto, madam Hua Chunying, kakakin ma'aikatar harkoin wajen kasar Sin ta bayyana a wani taron manema labaru da aka shirya yau Alhamis cewar, yawan kudin da kasar Sin ta kashe a bangaren aikin soja a shekarar 2014 bai kai kashi 1.5 cikin kashi dari ba bisa jimillar GDP ta kasar, ba ma kawai ya yi kasa da na sauran muhimman kasashen duniya ba, har ma bai kai matsakaicin matsayi na kashi 2.6 cikin kashi dari na duk duniya ba.

Game da batutuwan kudin da kasar ke kashewa a bangaren aikin soja da karfin rundunar sojan kasar Sin da suke jawo hankulan sauran kasashen duniya, madam Hua Chunying ta jaddada cewa, kasar Sin na tsayawa tsayin daka kan matsayin neman ci gaba cikin lumana da manufar tsaron kasarta. Makasudin bunkasa aikin sojan kasar Sin shi ne tabbatar da dinkuwar kasar Sin gaba daya da cikakken yankunan kasar da kuma biyan bukatun neman ci gaba a yayin da take kokarin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a wasu yankunan shiyya-shiyya, har ma a duniya baki daya. Kasar Sin ta bunkasa aikin sojanta ne ba domin kawo barazana ga kowace kasa ba. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China