in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Sin ya yi kira ga bunkasa zamantakewar al'ummar kasa da kasa cikin adalci
2015-02-10 16:15:30 cri
Mataimakin zaunannen wakilin Sin dake MDD Wang Min, ya ce kamata ya yi kasashen duniya su yi amfani da wannan lokaci na cika shekaru 70 da kafuwar MDD, wajen sa kaimi ga kafa tsarin bunkasar zamantakewar al'ummar kasashen duniya cikin adalci, da hakuri da juna, cikin yanayi mai dorewa.

Wang Min wanda ya bayyana hakan cikin jawabin sa ga taron kwamitin raya zamantakewar al'umma na MDD, ya kara da cewa kasashen duniya na fuskantar sabbin kalubale, da matsaloli, a kokarin su na bunkasa zamantakewar al'umma.

Ya ce, ya dace a sa kaimi ga bunkasar zamantakewar al'ummar duniya cikin adalci da cimma moriyar juna, da kiyaye muhalli, da samun bunkasuwa mai dorewa, da binciko sabbin dabaru, da hakuri da juna, a lokacin da ake kara samun bunkasar zamantakewar al'ummacikin daidaituwa.

Haka zalika, Wang Min ya bayyana cewa, Sin ta yi imani da kara samun ci gaba a sha'anin samun bunkasuwa, ciki har da fannin zamantakewar al'umma. Har wa yau za ta ci gaba da more fasahohin ci gaba tare da sauran kasashen duniya, da kara samar da damar hakan ga duniya, domin samun wadata a kasar Sin da ma duniya baki daya. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China