in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kaddamar da taron manyan jami'an dandalin tattaunawa kan hadin gwiwar Sin da Afirka karo na 10 a kasar Afirka ta Kudu
2014-12-10 10:03:33 cri
A jiya ne aka kaddamar da taron manyan jami'an dandalin tattaunawa kan hadin gwiwar Sin da Afirka karo na 10 a birnin Pretoria dake kasar Afirka ta Kudu. Yayin bikin kaddamar da taron, mataimakin ministan harkokin wajen kasar Sin Zhang Ming ya bayyana cewa, tun lokacin da aka kafa dandalin tattaunawa kan hadin gwiwar Sin da Afirka a shekarar 2000, ake fuskantar kalubale da dama, da kokarin kara shigar da kasashe a cikin dandalin tattaunawar, da kara kyautata tsarin dandalin, tsarin jagorancin dandalin da sa kaimi ga bunkasa dangantakar dake tsakanin Sin da Afirka a dukkan fannoni cikin sauri.

Yayin da yake yi bayani kan sakamakon da aka samu daga hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Afirka, Zhang Ming ya bayyana cewa, yawan kudin da aka samu a harkokin ciniki a tsakanin Sin da Afirka ya karu cikin sauri, inda a shekarar 2013 ya kai dala biliyan 210, wanda ya ninka sau 21 bisa na shekarar 2000. Kana an samu saurin bunkasuwar hadin gwiwa a tsakanin Sin da Afirka a fannonin zuba jari da tattara kudi, sannan an gudanar da ayyukan hadin gwiwa a tsakaninsu a fadin nahiyar Afirka. An kuma yi mu'amala sosai a tsakanin jama'ar Sin da Afirka, yawan Sinawa da suka ziyarci kasashen Afirka a shekarar 2013 ya kai miliyan 1 da dubu 895, kana yawan 'yan kasashen Afirka da suka zo kasar Sin ziyara a shekarar ya kai dubu 553.

Hakazalika kuma, Zhang Ming ya jaddada cewa, shekarar badi shekara ce da cika shekaru 15 da kafa dandalin tattaunawa a tsakanin Sin da Afirka, kasar Sin tana fatan ita da bangaren Afirka za su gudanar da taron ministoci karo na 6 na dandalin tattaunawar yadda ya kamata, da kara inganta sabuwar dangantakar abokantaka a tsakaninsu zuwa wani sabon matsayi. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China