in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon ya yi kira ga bangarori daban daban na kasar Yemen da su martaba shawarwin zaman lafiya
2015-02-09 15:52:57 cri
Babban sakataren MDD Ban Ki-moon ya bayar da sanarwa ta hanyar kakakinsa a ranar 8 ga wata, inda ya yi maraba da shawarwari kan batun kasar Yemen da za a gudana ba da dadewa ba, kana ya yi kira ga bangarori daban daban na kasar da su nuna sahihanci da martaba juna a yayin shawarwarin zaman lafiya.

Sanarwar ta bayyana cewa, mashawarcin musamman na babban sakataren MDD Jamal Benomar zai sake yin kira ga bangarori daban daban da batun kasar Yemen ya shafa da su yi shawarwari a ranar 9 ga wata, Ban Ki-moon ya yi maraba da wannan batu, tare da kalubalantar bangarorin da su yi hadin gwiwa tare da Jamal Benomar domin nuna dattako a gun shawarwarin.

Kungiyar dakarun Houthi ta darikar Shi'a ta kasar Yemen ta sanar da kafa kwamitin kula da harkokin shugaban kasar da majalisar gudanarwa ta wucin gadi ta kasar a ranar 6 ga wata, don maye gurbin shugaban kasar na yanzu da majalisar dokokin kasar da gudanar da harkokin kasar. Matakin na kungiyar Houthi ya sanya kasar cikin wani halin rudani da rashin tabbas game da rashin wata gwamnatin kasar mai cikakken iko. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China