in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
IMF ta sanar da kafa asusun samar da taimako ga wadanda bala'i ya aukawa
2015-02-06 11:06:22 cri
Asusun bada lamuni na duniya IMF, ya sanar da kafa wani asusun da zai samar da taimako ga wadanda bala'i ya aukawa. Har wa yau asusun zai samar da soke basussuka da suka kai na kimanin dala miliyan 100, da ake bin kasashe uku mafi fama da cutar Ebola a yammacin Afirka.

IMF ya ce yana da nufin samar da gudummawar kudi, ga kasashe masu fama da talauci dake fuskantar manyan bala'u, ko cututtuka, da rage basussukan da ake bin su, a wani mataki na taimakawa kasashen ta yadda za su samu damar amfani da albarkatunsu wajen yaki da bala'i, da kuma sake gina kasa bayan aukuwar hakan.

Majalisar IMF ta tsaida kudurin cewa, asusun samar da taimakon zai soke basussuka kimanin dala miliyan 100 da ake bin kasashen Liberia, da Saliyo da Guinea, bisa kudurin na tallafa musu biya basussuka.

Bugu da kari, majalisar IMF tana da shirin samar da rancen-gata da ya kai dala miliyan 160 ga wadannan kasashe uku. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China