Cikin sakon nasa, shugaba Xi ya ce zumuncin gargajiya tsakanin jama'ar kasar Sin da na kasar Zambia na ci gaba da kyautata, yayin da aka samu managarcin sakamako a fannin hadin gwiwar kasashen biyu.
Shugaba Xi ya kara da cewa kasarsa na kara mai da hankali sosai game da bunkasar dangantakar abokantaka tsakaninta da Zambia, tana kuma fatan ci gaba da karfafa hadin gwiwar kasashen yadda ya kamata, a wani mataki na kara inganta zaman rayuwar al'ummomin kasashen. (Maryam)