in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dan takarar jam'iyya mai mulki a Zambia ya lashe zaben shugaban kasa
2015-01-25 17:22:25 cri
Jiya Asabar 24 ga wata, kwamitin kula da harkokin zaben kasa na Zambia ya sanar da cewa, dan takarar jam'iyya mai mulkin kasa ta Patriotic Front Edgar Lungu ya lashe zaben shugaban kasa, wanda zai kasance shugaba na shida na kasar Zambia bayan da kasar ta samu 'yancin kai a shekarar 1964.

A yayin taron manema labaran da aka shirya, mukaddashin babban alkalin kasar ya bayyana cewa, yawan mutanen da suka kada kuri'u a yayin zaben shugaban kasa a wanann karon ya kai kashi 32.36 bisa 100, adadin da ya kasa da na zaben shugaban kasa na karon da ya gabata, dake kashi 50 bisa 100.

Haka kuma a yayin wani taron manema labarai, dan takarar kawancen adawa na UPND, Hakainde Hichilema ya bayyana cewa, sakamakon zaben gaskiya bai nuna fatan al'ummar kasar ba, tare zargin jam'iyyar mai mulki da tafka magudi a yayin zaben.

Dangane da lamarin, shugaban kwamitin kula da harkokin zaben kasa ya bayyana cewa, an taba canja lokacin yin kididdigar kuri'u da aka kada sabo da dalilin dake shafar yanayi, amma babu shakka an gudanar da babban zaben shugaban kasa na wannan karo ba tare da boye kome ba da kuma cikin yanayin adalci. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China