in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Sin ya aika da sakon ta'aziyar rasuwar shugaban Zambiya
2014-10-30 20:37:37 cri
A yau Alhamis 30 ga wata ne, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya aika da sakon ta'aziyya ga shugaban rikon kwarya na kasar Zambia Guy Scott dangane da rasuwar shugaba Michael Sata na kasar, inda a madadin gwamnatin kasar da jama'arta, shugaba Xi ya mika ta'aziyya dangane da rasuwar marigayi shugaba Sata, tare da jajantawa iyalansa.

A cikin sakon, shugaba Xi ya bayyana cewa, a tsawon rayuwarsa, shugaba Sata ya dora muhimmanci kan bunkasa dangantakar abokantaka da hadin gwiwa tsakanin Sin da Zambia. A lokacin da ya ke shugabancin kasar, an kara sada zumunci da karfafa hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu yadda ya kamata.

Shugaba Xi ya kara da cewa, Sin ta dora muhimmanci kan raya dangantaka tsakanin kasashen biyu. Kuma ya yi imani cewa, bisa kokarin gwamnatoci da jama'ar kasashen biyu ke yi, za a kara samun kyaututuwar kyakkyawar dangantaka da dankon zumunci a tsakaninsu.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China